Featured

BUHARI BA SHUGABA BANE — Bello Muhammad Sharada

Muna rokon Allah Ta’ala kada ya maimaita mana mulki irin na Buhari da Jonathan, Allah Ta’ala ya bamu jagora a kasa da jihohi 36 har Abuja da kananan hukumomi 774 masu alheri da za su tausaya mana, su kalli matsalolinmu, su yi bakin kokari wajen shawo kansu da magancesu.

“Rabbana akrijna min hazihil Qaryatil zalimi ahalulaha, wajaalanna min ladunka waliyyan wa jaalna min ladunka nasira.”

Jiya mahara, wato miyagun daji a kan babura kusan mutum 300 suka shammaci motocin rakiyar shugaban kasa akan hanya. Sun fito daga Abuja zuwa Daura, inda PMB zai yi hutu da shagalin salla. Suka bude musu wuta, a sanadin haka suka kashe mataimakin kwamishinan ‘yan sanda.

Jiya wajen karfe goman dare, wasu gungun mahara da adadi mai yawa suka fasa gidan kurkuku na Kuje da ke Abuja. Akwai furusuna 994 a ciki, da shiga sun tarwatsa fursunonin, har mutum 600 sun gudu. A cikin wadanda ake tsare da su har da gogaggun ‘yan Boko Haram ko ISWAP/Ansaru su 64.

A sati guda da ya gabata a jihar Neja a karamar hukumar Shiroro, shugaban kasa Muhammad Buhari yana kasar Portugal aka kaiwa sojan Najeriya farmaki aka kashe sojoji 30 da mobayil bakwai da yan bijilan. Haka shugaba Buhari yana kasar Spain aka kai hari coci a Owo ta Ondo aka kashe mutum 40. Tun daga watan Janairu 2022 babu watan da ya zo Buhari bai fita waje ba. Yana wajen kuma za a kashe tai, sai dai ya aiko da gaisuwa da ta’aziyya.

Abin takaici da Allah Wadarai duk da munin wannan ta’adda da aka yi jiya a Kuje da Dutsinma a Abuja da Katsina, amma shugaban kasa ya hau jirgin sama da tawaga ya tafi kasar Senegal. Zancen da muke yanzu ya kusa isa can.

Nan fa a Najeriya ana jimami, ana fargaba, ana sallallami, ana tashin hankali ko a jikin Buhari, to me zamu yi da Buhari, wallahi Buhari ba shugaba bane, kuma bama yinsa. Mun yi tir da halinsa da halin ko in kula da yake yi wa al’ummar kasar nan.

A da nakan ce, ministan tsaro Bashir Magashi da ministan cikin gida Abdurauf Aregbesola da National Security Adviser Babagana Munguno su yi murabus, su bar kujerunsu, abin takaici ne zamansu. Yanzu kamata ya yi ‘yan majalisar dattijai su tankado keyar Buhari tun lokacinsa bai cika ba ya fado. Su wurgo shi daga kan kujerar mulki, su hantsilo da shi, sai mu ga ta inda zai rika yawo a Kaduna ko Abuja ko Daura.

BUHARI BA SHUGABA BANE

Qalubale

Featured

Bayan shekaru bakwai, Ganduje ya dawo da biyan garatuti

Gwamnatin jihar Kano, karkashin maigirma Gwamna Ganduje, ta dawo da biyan garatuti, bayan wata yarjejeniya da ta cimma da shugabannin hukumar fansho ta jiha, cewa zata dinga bada wani kaso na kudin kowane wata domin a dinga ragewa tsoffin ma’aikatan hakkin su.

Tsarin biyan garatutin, kamar yadda shugabannin su ka tsara, duba da karancin kudin da yake hannu kuma ga yawan jama’a da su ke a kasa, shugabannin sun yanke shawarar biya daga inda aka tsaya tun a baya, wato shekarar 2016.

Haka kuma duk wanda kudin garatuti din sa bai haura miliyan biyu da rabi (#2.5m) ba, zai sami kudin sa gaba daya Insha Allah!

Wanda kudin sa ya haura (#2.5m) shine zai sami wani kaso na kudin, wato (part payment), shima kuma duk lokacin da za’ayi biya na gaba sunan sa zai sake fitowa har a gama biyan sa.

Muna addu’a Allah ya kiyaye tunanin gwamnati ta ci gaba da alkawarin da ta dauka na bada kudin duk wata-wata

Wadanda Allah ya sa su ka sami nasu, muna addu’a Allah ya sanya albarka a cikin kudin.

Qalubale

Featured

Yaushe Abba Kyari ya koma bakin aiki bayan an dakatar da shi

Harkar tsaro a Najeriya abar tuhuma ce – dalili na shine, kowa ya san an dakatar da Abba Kyari daga wannan aiki a hukunce, har zuwa wannan rana da muka buga wannan labari babu lokacin da wani ya ji cewa an maida shi bakin aiki a hukunce, wane dalili ne ya ba Abba Kyari damar komawa bakin aiki?

Wannan harkalla fa kamar yadda labarin ya zo, anyi ta ne daga watan Janairu zuwa wannan rana da muke buga wannan labari – ko dai akwai sa hannun wadanda bamu gani da idanuwan mu a wannan harkalla – order from above?

Yaushe Abba Kyari ya koma bakin aiki bayan an dakatar da shi, har ya sami damar yin wata sabuwar harkalla?

A ra’ayin wasu mutane su na cewa, ta bayan fage ya koma bakin aikin nasa sakamakon yaransa har yanzu su na yin biyayya a gareshi kuma su na ba shi bayanan sirri na abinda ke faruwa a ofis – shi kuma yana basu shawarar yadda za su tinkari aikin nasu.

Hakane ko ba haka bane, ya rage bincike ya tabbatar kuma a sanar da jama’a yadda akayi Abba Kyari ya tafka wannan harkalla da sunan aikin da tuntuni aka dakatar da shi, ko kuma dai daga sama ne aka daure masa gindin yin aiki ta bayan fage, bayan kuma ga shugaban da ya maye gurbin sa amma ba’a yin aikin dashi – idan ba haka ba ne, me yasa su shugabanninin NDLEA su ka saurari wanda ba ya kan kujera domin yin wata alakar aiki dashi?

https://t.co/kKZ1ap66dZ

Radio BBCHausa sun riwaito cewa, shi Abba Kyari da ake tuhuma yayi magana da jami’an NDLEA a aikace kuma a hukunce, har ma ya bukaci jami’an NDLEA din su karbi masu laifi daga hannun su, ma’ana dai suyi handover kenan daga hukumar tsaro ta yan sanda zuwa ga hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi.

Idan wannan zarge-zarge sun tabbata, ko shakka babu an fara gano musabbabin abinda ya jawo rashin tsaro kenan a Najeriya – kamar yadda masana sukayi sharhi cewa, duk matsalolin tsaro a Najeriya ya samo asali ne ta hanyar sha da fataucin miyagun kwayoyi.

Qalubale

Featured

Gwamnati mai son ta gama lafiya sai ta biya hakkin al’umma

Bayan kammala aikin bautawa jihar Kano tsayin shekaru 35 – wasu ma duk sun mutu da bakin ciki, zuwa yanzu dai gwamnatin Kano ta gaza biyan ‘yan fansho hakkokinsu tun shekarar 2016

Abin mamaki kuma, sai gashi majalisar dokokin jihar Kano ta sahalewa Maigirma Gwamna Ganduje kudade har miliyan 500 domin ayi wa gadar kofar ruwa ado, bayan an kammala gadar lafiya kalau, amma an sake ware wadannan madudan kudade domin kawata ta.

Shugabannin hukumar fansho ta jiha tace, tana bin gwamnatin Kano bashin hakkokin ‘yan fansho na garatuti fiye da Naira Miliyan Dubu Ashirin da Takwas (#28bn)

Masu iya magana dai sunce komai girman gona tana da kunyar karshe!

Qalubale

Featured

Shugaba Buhari ya kaddamar da Dalar Shinkafa

Talata 18 ga watan Janairu, Shugaban Kasar Najeriya Muhammad Buhari ya kaddamar da Dalar Shinkafa, wannan yana daga cikin kudurorin shugaba Buhari na samar da Kasa mai dogaro da kanta masamman ta fannin abinci.

Buhari ya kaddamar da Dalar Shinkafar ne a birnin Abuja inda kamfanoni masu zaman kansu mallakin ‘yan Najeriya su ka baje kolin irin shinkafar da suke samarwa domin ciyar da Kasa da kuma tabbatar da ‘yan Najeriya sun dogara da kansu wajen noma isasshen abincin da za’a dogara da shi batare da dogaro da kasashen ketare ba.

Abinda ya ragewa talakawa su gani shine, Gwamnati ta tsaya tsayin daka domin ganin abincin yana isa ga masu bukata a cikin Kasar, har sai ya wadaci jama’a kafin a fitar dashi ketare domin siyarwa.

Haka kuma Gwamnati ta sa idon ga masu yin simogal domin fitar da abincin kamar yadda ta sa Ido wajen shigowa da shi, a baya dai Gwamnatin ta ce, Fasakwaurin Shinkafa Haramun Ne yin hakan zai takaita ko ma ya hana tsadar da talakawa ke fama da ita a halin da ake ciki yanzu.

Allah ya ba shugabannin mu ikon yin amfani da irin wannan abinci da ake samar wa a Nageria a gidajen su.

Qalubale

Featured

SIYASA BA DA GABA BA

Gwamna Ganduje tare da rakiyar tsohon Shugaban jamiyyar APC na Kano Malam Abdullahi Abbas sun kaiwa Sabon shugaban Jamiyyar APC na Kano Amb Ahmadu Haruna Danzago ziyarar ta’aziyyar rashin yayansa da yayi a yau.

Gwamna mun gode, Former chairman mun gode, Masu dauka da zafi sai a fadaka!

Daga Ayman Ado

Qalubale

Featured

Bagudu approves N6 Billion for the payment of gratuity

Press Release

The Kebbi State Governor, Senator Abubakar Atiku Bagudu has graciously approved the release of 6 billion Naira for the payment of State, Local Government and LGEA workers gratuity. Retired workers who disengaged from service in 2017 and 2018 and had received part payment of their gratuity will be paid their remaining balance. While other retirees from 2019,2020 and 2021 will also receive payment of their gratuity.

This happy development was part of the outcome of an earlier meeting today between the Chairman, Audit Committee for State and Local Government Pensioners, Acting Head of the Civil Service and the state Chairman, NLC.

It was unanimously agreed that labour Unions and the Nigeria Union of Pensioners should be involved in all stages in the preparation and payment of gratuity to the deserving retirees.

This is to ensure probity and accountability in the process of payment.

This announcement is contained in a statement signed by the Acting Head of Service, Alhaji Safiyanu Garba Bena and made available to the newsmen on Friday.

The statement further stated that, the invaluable gesture of the governor is in line with his administration’s policy and aspiration towards improving the general welfare of the retired workers in the state.

Arrangements for the payment will commence as from next week Monday, the 17th of January, 2022.

Signed,

YAHAYA SARKI,
Special Adviser (SA) Media to Kebbi State Governor
14/1/2022

Qalubale

Dangote Refinery: Time to dismantle your depots, sell them as scraps – Otedola to oil importers

My Dear Brother Aliko,

First and foremost, I want to extend my heartfelt congratulations to President Bola Tinubu for his unwavering support and belief in actualizing this monumental achievement under his administration. This day belongs to every Nigerian who has dared to dream of a better future. Congratulations to our great nation—today, we all stand a little taller.

Aliko, it feels like just yesterday, but it has been 25 long years since we first set our sights on transforming Nigeria’s energy landscape. I remember vividly when we set up the Blue Star Consortium to acquire stakes in the Kaduna and Port Harcourt refineries—20% for me and 51% for you. We were ready to change the game, but fate had other plans. The government of the day, in an act I can only describe as utterly obnoxious, canceled our stakes and thwarted our vision. But, as always, you refused to be deterred.

You never gave up on the dream we shared. You carried the torch forward, igniting a spark that has today become a roaring flame. And now, 25 years later, here we stand on the precipice of history, with the first fuel shipment from the Dangote Refinery—a feat that is nothing short of miraculous.

While the Kaduna and Port Harcourt refineries have remained dormant, their promise unfulfilled despite billions of dollars spent on so-called turn-around maintenance, you have achieved what many said was impossible. You have beaten all the skeptics, silenced the naysayers, and proved wrong those who doubted your resolve, even those who never wanted this project to succeed.

You have not just built a refinery; you have liberated us from the chains of economic dependence that have held this nation back for far too long. The days of bowing to foreign powers for our fuel needs are over, thanks to your vision and determination. You have dealt a death blow to the so-called local cabals who have fattened themselves for years, feeding off our nation’s economic slavery. These cabals, who have grown rich by keeping Nigeria in a perpetual state of dependence, must now face the reality that their era of easy gains is coming to an end.

I am reminded of the time you revolutionized the cement industry in Nigeria. Ships that once brought in cement turned into rusting relics, scraps of a bygone era. Now, with your refinery in full swing, I foresee a similar fate for fuel imports. The depot owners should take heed—it’s time to dismantle those depots and sell them as scraps while the market is still high. The world has changed, and those who do not adapt will be left behind.

When I ventured into the depot business with Zenon, it was in response to the inefficiencies of the NNPC. Zenon pioneered the diesel business in Nigeria and quickly became the largest in the country, filling the gaps left by our inefficient system. But today, your refinery stands as a beacon of what is possible when one has the audacity to dream and the tenacity to see it through.

Aliko, you have my deepest admiration and respect. Congratulations to you and the entire board, management and staff of Dangote Refinery on this monumental achievement. This is not just a victory for you but for every Nigerian who dares to dream. May this be just the beginning of even greater things to come.

With profound respect and warmest regards,

F. Ote$

Tattaunawa ta masamman da BIRNIN ZUCIYA

Group din WhatsApp mai suna BIRNIN ZUCIYA karkashin jagorancin Dr Abba Nura yayi tunani wajen hada kuɗi domin ciyarwa ga masu bukata a cikin Ramadan a wannan shekara.

Kamar yadda muka zanta da wanda ya kirkiri group din na BIRNIN ZUCIYA Alh. Ibrahim Ali Ahmad wanda akafi sani da (Mu’azzam) ya sanar da kafar sadarwa ta Qalubale yadda aka kafa wannan group kuma menene dalilin kafashi da kuma manufofinsa?

As-salamu alaykum warahamatullah wabarakatuh, da farko muna godiya ga Allah daya bamu dama domin gabatar da wannan tattaunawa a wannan rana ta Lahadi 7 ga watan Afrilu 2024 wacce tazo daidai da 28 ga watan Ramadan 1445 AH

Kai tsaye, kamar yadda mai gabatarwa ya tambaya, zan bayyanawa duniya cewa wannan group na WhatsApp mai suna BIRNIN ZUCIYA an kirkireshi ranar Alhamis 28/5/2020 bisa dalilai kamr haka;

❤️ *BIRNIN ZUCIYA GROUP*
*MANUFOFIN WANNAN GIDA*
An bude wannan gida ne mai suna *BIRNIN ZUCIYA* domin sada zumunci, fadakarwa, ilimantarwa, taimakon juna da kuma kawo abubuwa da suka shafi al’amura na yau da kullum – bisa mutumtaka da girmamawa, duk tsokana da muke yi wa junanmu, mu dauka raha ne, ba gaskiya ba ne – laifi ne cin fuska ko cin zarafi a wannan gida.
❤️ NISHADANTARWA
* FADAKARWA
* ILIMANTARWA
* RAHA/ZOLAYA
* SADA ZUMUNCI
* TAIMAKON JUNA
*SHIRYE-SHIRYEN DA MUKE GABATARWA*
(Programs)
*1. KIWON LAFIYA*
*2. RAYUWA A MUSULUNCI*
*3. TAURARON MAKO*
*4. FADAKARWA GA MA’AURATA*
*5. INA MUKA DOSA*
*Wasu shirye-shiryen nanan tafe nangaba insha Allahu, Allah yabamu nasara Ameen*
✍️ DOKOKIN WANNAN GROUP
1. ✅ Ba’a sanya videos, hotuna ko furuci na batsa.
2. ✅ Mu kiyaye mutuncin junan mu, ta hanyar girmama junanmu da daraja kalamai.
3. ✅ Dokane cin zarafin wani ko zaginsa ko yin fada, in wani yayimaka ka sanarwa shuwagabannin gidan zasudauki mataki.
4. ✅ Kada ka tursasa wani ya amince da tunanin ka ko ra’ayin ka.
5. ✅ Dokarmu tahana dauko zancen wani gida zuwa wannan gida ko zancen gidan mu zuwa wani gida.
6. ✅ Wajibi ne mambobi su dinga amsa sallama, sannan su dinga yin magana a group akai-akai, musanman insuna Online ko in ana gabatarda shiri suyi liking.
7. ✅ Munhana tallace-tallace ko tallen kaya kona group a cikin wannan gida.
8. ✅ Mun haramta tattauna maganar siyasa, Jam’iyya, ko batun akidar addini, ko kwallo, ko yin posting game dasu.
9. ✅ Laifi ne kawo saɓani daya hada ku a wajen group zuwa cikin wannan group.
10. ✅ Dolene mu kasance masu kiyaye wadannan dokoki tareda mutunta shugabancin wannan gida, zaka iya kawo shawarar duk wani abinda zai kawo cigaban wannan gida ko mutanan cikinsa.
11. ✅ Za’a iya yin gyara a wadannan dokoki a duk lokacin da bukatar haka ta taso.
Muna maraba da dukkan gudumuwar mambobin wannan gida ta kowanne bangare.
Allah yabamu nasara yakara hada kawunanmu Ameen.
✍️ Shuwagabannin wannan gida su ka rubuta.

Kamar yadda Alh Ibrahim Ali Ahmad (Mu’azzam) yayi cikakken bayani tun daga ranar da aka kafa wannan group, haka kuma yayi bayani na dalilai na kafawa da kuma manufofin kafawar, har ma da abubuwan da group din ke gabatarwa domin amfanuwar jama’a.

Zamu so jin yadda ciyarwar Ramadan ta gudana inda Mu’azzam ya sake yin bayani kamr haka;

Mun samar da kudi ne ta hanyar yin karo-karo da group din BIRNIN ZUCIYA ya nemi shugabanni da mambobi su bayar domin a gudanar da wannan aikin alkhairi da sunan wannan group, ba tare da bata lokaci ba, dayawa suka karbi kiran kuma suka bayar da abinda zasu iya bayarwa

Gombe

Kamar yadda muka ga hotuna da videos, group din BIRNIN ZUCIYA yayi namijin kokari wajen samar da abin buda baki ga masu azumi a wasu jihohi guda biyu Yobe da Gombe.

Yobe

Alh Mu’azzam wane dalili yasa aka gabatar da wannan ciyarwa a jihohi daban daban?

Dalilin mai sauki ne, duk wani group na social media Yana kunsar mutane daga jihohi daban-daban, wani lokaci ma zakaga har da mutane daga makwabtan kasashe kamar su Chad, Niger, Libya da dai sauransu.

Wannan dalili yasa muka dauki jihohi biyu domin mu fara dasu, kasancewar akwai mambobin mu a jihohi sai muka tuntubesu su ka amince muka basu amanar yin wannan aiki da sunan group din BIRNIN ZUCIYA, mun tura masu kudaden da aka tara kuma sun aiwatar da abinda ya dace, sannan shugabancin group da mambobi sunji dadin yadda aka tsara kuma aka gudanar da abin cikin sauki.

Gombe
Yobe

Alh. Mu’azzam, zuwa yanzu mambobin group sunkai nawa?

Zamu so jin su waye shuwagabanni a group din BIRNIN ZUCIYA

A halin yanzu shugabanni 14 muke da su, sai kuma idan an hada su da MAMBOBI anyi jimla, gaba daya mu dari da goma sha daya (111) gasu kamar haka;

Chairman – Dr Nura Abba
Vice Chairman – Hajiya Fattu Khalid Usman
Secretary – Alh. Rabi’u (My Fans)
Deputy secretary – Muhammad Bukar
PRO l – Omar Farouk Sani Fagge
PRO ll – Malam Ibrahim Khalil (Sardauna)
Woman Leader – Hajiya Fatima (Hajiyan Kabo)
Deputy Woman Leader – Hajiya Fatima (Maman Islam)
Welfare Officer l – Hajiya Zainab (Anty Zee)
Welfare Officer ll – Musa Sani
Financial Secretary – Manu Ali Bima
Treasurer – Ibrahim Ali Ahmad (MU’AZZAM)
Auditor – Baba Balarabe
Chief Whip – Alh Rabi’u (Dee Rabs)

Akwai kwamatin amintattu masu ruwa da tsaki a cikin wannan tafiya, wadanda muke kira Board of Trustees (BoT)

Wannan kwamati nine nake jagorantarsu a matsayina na Chairman sai kuma mataimakina Haruna Ibrahim

Yanzu haka wannan gida ya tafi shekara 4 da kafawa, gashi kai ɗaya nasamu a office domin amsa tambayoyin mu, shin a tsayin wannan lokaci wace nasara wannan group na BIRNIN ZUCIYA ya samu kuma wane abu yafi baka jin dadi bisa samar da wannan gida zuwa yanzu?

Gaskiya mun sami nasarori masu tarin yawa duba da yadda muka shafe shekaru hudu cikin mutumtaka da girmamawa batare da samun tashin hankali ba.

Abu na biyu shine yadda muke gabatar da shirye-shiryen da suke amfanar da jama’ar gidan

Abu na uku shine yadda muka kulla zumunci tun muna ganin juna a hoto, har yakai muna iya zuwa garuruwa ko unguwannin junanmu domin sada zumunci

Sai kuma wannan ciyarwa da mukayi a wannan wata na Ramadan, shine babban abinda yafi bani dadi a duk tsayin wadannan shekarun

Alh. Mu’azzam jagoran wannan tafiya ta BIRNIN ZUCIYA, bamu sani ba, ko akwai wani danasani da kayi bayan ka kirkiri wannan tafiya?

Har ka bani dariya, maganar gaskiya tun bayan kirkirar wannan gida zuwa yanzu shekara hudu, babu wani danasani, sai jin dadi da farin ciki

Amma akwai abubuwan da bazan manta dasu ba, na farko dai mun hadu da mutane, inda duk ka tara mutane dole akwai zaman hakuri, sakamakon mabanbantan tunani da za’a samu, a halin yanzu akwai mutane da muka zauna dasu a wannan gida kuma basanan tare damua wannan gida, sakamakon haka har yanzu muna tare dasu a gefe guda muna sada zumunci.

Wasu mata ne, sunyi aure, kuma sun bada gudunmawa matuka wajen cigaban gidan da dorewarsa, muna yi masu fatan alkhairi, Allah ya zaunar dasu lafiya a gidajen aurensu.

Daga karshe, wace shawara zaka ba shugabanni da mambobi har da ma sauran masu ire-iren waɗannan gidaje a kafar sadarwa ta zamani?

Alhamdulillah shawarwarin da zan baiwa shugabanni da mambobi sune;

Na farko duk abinda za’ayi a irin waɗannan gidaje a dora shi bisa doron niyyar yin abin domin Allah, sannan a nufi Allah yayi jagora, sai kuma taimako ga dukkanin ma’abota gidan, ta hanyar ilimantarwa, fadakarwa da duk wani abu da zai kawo cigabansu

Na biyu, a dinga mutunta juna, a girmama juna, a tausasa kalamai ga juna

Na uku, a dinga yin hakuri da juna idan wani yayi wani abu wanda ya sabawa dokokin gidan a fahimtar dashi kuskuren daya aikata a cikin masalaha

Na hudu, duk wata rashin fahimta data shafi tsakanin ƴaƴan group su kwantar da hankalinsu kuma su sanar da shugabanni, su kuma shugabanni suyi gaggawar daukar matakin warware matsalar cikin ruwan sanyi

Allah ya bamu dacewa, ya karo mana cigaba da walwala a rayuwarmu, Allah ya zaunar damu lafiya, ya zaunar da kasarmu lafiya, Allah ya kyautata zuriyarmu, ciyarwa da wannan gida yayi a wannan wata mai albarka na Ramadan Allah yasa a mizani, ya hada mu cikin ladan gaba daya.

Alh. Mu’azzam muna godiya da wannan lokaci da ka bamu, sai wani lokaci idan bukatar haka ta taso.

NLC Kano Branch on attempt of salary deduction

Kano State Government’s attempt to deduct the workers’ salary for the month of February, 2022

On Monday 28/2/2022 late Night i received a call from the Office of the Head of service through Director Salary and wages requesting for the JCF Chairman to attend a meeting on Tuesday 1/3/2022 by 2:00pm at the office of the Head of service and i asked him for the reason of the meeting but he couldn’t give.


Few minutes later, a text message was received from the Chairman NLC Kano branch requesting for the JCF Chairman and Secretary to attend a joint meeting of Labour Unions of Kano State on Tuesday 1/3/2022, by 12:30pm at NLC Secretariat Kano state.

During the meeting, members in attendance from different labour Unions discussed and hypothesed on the reason for requesting the labour Unions’ meeting at the office of the Head of service on that day.

The JCF at the meeting boldly eared it’s position on no single kobo be deducted from the salary of its Members, we also narrated to the larger house that for good three 3years Govt don’t pay or add annual increment to our members’ salary.


In the same vein, we attended the meeting with the Head of service, Commissioner of Finance and other Permanent secretaries and directors and during the meeting they made a narration where they notified the labour Unions leaders here present at the meeting that, Kano state Govt don’t have sufficient funds to pay full salary of February, 2022 to Kano state workers do to the short fall of Federal Government allocation (FAAC) as they said. The labour Unions leaders under the leadership of NLC Chairman inform the meeting that, we the labour Unions will going back and inform the larger house for taking a decision on the issue.


On Wednesday 2/3/2022 we meet at the NLC Secretariat by 11:00 for another discussions and decisions, however, in the meeting we jointly resolved that, the workers don’t agreed to sacrifice a single kobo from their salary, and a press conference will be hold to inform the workers and public the position of Labour Unions on the issue, likewise a prayer sessions will be organized to request for Allah’s intervention on the issue.


The joint labour Unions re attend the meeting with the Kano State Govt representatives again on Wednesday 2/3/2020 and notified its position as decided during the morning meeting of joint labour Unions. Finally the govt representatives stand on their feet of using April 2021salary table to release the February, 2022 salary.
Today Thursday, 3/3/2022 a press conference will be hold by 11:00am at the NLC Secretariat to inform the public and workers the position of Labour Unions.

Thanks

Qalubale

BUHARI MAI ABIN MAMAKI

Yanzu na samu labarin Shugaban kasa Muhammad Buhari ya aika wa majalisar kasa takardar cewa ba zai sa hannu akan sabuwar Dokar Zabe ta 2021.

Sai da shugaba Muhammad Buhari ya yi kwana talatin cur sannan ya mayar da amsa ga majalisar kasa kan sabuwar dokar zabe ta “Electoral Bill 2021”

An yi ta nuku-nuku da kumbiya- kumbiya, don a biya wa gwamnoni bukatarsu. Gwamnoni sun yi nasara, burinsu ya cika, mutanen Najeriya sun yi asara.

Alkawarin da PMB ya dauka zai bar gadon sahihin tsari na zabe da shugabanni ya fadi kasa warwas.

A tsaro mun fadi. A tattalin arziki mun fadi. A dimokuradiyya mun fadi.

Duk dalilai da shugaban kasa Muhammad Buhari ya dogara da su don fatali da wannan gyararriyar dokar, an gina su a gurguwar fahimta.

Wannan matsayin ya dada tabbatar min da cewa BA SAITI AKA ZO A YI WA NAJERIYA BA.

A’a an zo a more kuma a hole.

Daga Bello Muhammad Sharada

qalubale.news.blog

Titin zuwa gidan Gwamnatin Jihar Kano yana cigaba da zama babbar Barazana ga al’umma.

Titin Gidan Gwamnatin jihar kano ya zama mafarka ‘Yan sara da suka, tare da masu kwacen wayoyin da dukiyar al’umma kuma hakan na nuna cewa idan gwamnati batai gaggawar magance matsalar ba wannan abu ka’iya hayayyafa, Domin kuwa wadansu bata gari suna fakewa da titin a matsayin babban titi mai tsaro wanda ba kowane zai gane da bata gari ba agun, suna tare mutane suyi musu fashi da makami.

Sau tari al’umma sun sha kokawa a game da wannan titin, kamar yadda wani bawan Allah da aka tareshi a lokacin da yake neman abun Hawa ya tafi gidansa ya bayyana mana…

“Idan mutum ya baro wajejen kofar Gidan Gomnati to fa komai ka’iya faruwa dashi, saboda a iya wajejenne kawai jami’an tsaro suke, Na taho ina tafiya ina neman baburin Adaidata sahu kwatsam sai ga wadansu matasa akalla sunkai su 6, da yake ankirani a wayata zan dauka, sukace inbasu wayar na kalli hannuwansu naga dukkansu da wukake na mika musu daya daga cikin su yace su lalube aljihunana suka lalabe kuma komai na ciki saida suka sacemin”

Mutane da dama sunsha kawo kukansu akan an taresu a wannan titin musamman daga karfe 7:30 zuwa 11:30 na dare a wannan titin.

Shin Meyasa Hakan ke faruwa?
Ta yaya za’a magance wannan matsalar?

Daga: 👉 Rabiu Tijjani Abubakar

Madogara: Kano Online News

Hukumar Fansho Ta Jihar Kano Na Bin Hukumomi Bashin #53bn

A wani gangamin taro da kungiyar fansho ta Jihar Kano ta shirya a Karamar Hukumar Kumbotso, wanda ya gudana a dakin taro na Islamic Centre da yake a Panshekara ranar Alhamis 8 ga watan Yuli, 2021

Shugaban kungiyar ya koka ta bakin mataimakinsa Alh Shu’aibu Musa Jibrin, masamman yadda ‘yan Fansho ke korafe-korafen rashin kula da hakkokinsu bayan ajiye aiki da sukayi, duba da cikarsu shekaru 35 suna aikin gwamnati kokuma cikarsu shekaru 60 da haihuwa.

Sha’aibu Musa Jibrin ya koka da yadda hukumomin gwamnati kimanin guda shida ke jan kafa wajen kin sauke nauyin da ya rataya a kansu kamar yadda dokar da ta kafa hukumar ta Fansho ta bayyana.

Dokar ta bukaci dukkanin ma’aikatun gwamnati su turawa hukumar ta Fansho kashi 8% da ake kwashewa daga albashin ma’aikatansu, sannan kuma su hada da kashi 17% na kason gwamnati na dukkanin yawan ma’aikatansu, su turawa hukumar Fansho

Wannan shine abinda ke gagarar ma’aikatun gwamnatin a Jihar ta Kano, inji Sha’aibu Musa Jibrin – ya kara da cewa yau kimanin shekaru 5 kenan hukumar Fansho ba ta iya biyan garatuti ga wadanda su ka bar aikin, gashi kuma ya fara shafar kudaden Fansho.

Shugaban ya ce dole ce tasa suka bude asusun ajiya guda biyu, daya na ‘yan Fanshon Jihar daya kuma na ‘yan Fanshon kananan hukumomi, domin zalincine ka dauki kudaden wadanda ke biyan kudadensu ga hukumar ta Fansho ka biya wadanda suke kasa biyan kason da ya wajaba a kansu.

Shine dalili da wasu ma’aikatan kananan hukumomi suke ganin an yanke ma su kudadensu na Fansho, wannan ya biyo bayan rashin turawa da kason kudaden da ma’aikatansu keyi ga hukumar ta Fansho.

Zuwa yanzu, hukumar Fansho ta jihar Kano na bin bashin hukumomin gwamnati kudaden da su ka kasa zubawa a aljihun hukumar Fansho fiye da zunzurutun kudi Naira biliyan Hamsin da Uku (#53bn)

Ita kuma hukumar ta Fansho zata iya biya dukkanin hakkokin garatutin ‘yan Fansho ne cikin kwanciyar hankali, idan ta mallaki Naira biliyan ashirin da bakwai zuwa da takwas (#28bn) a ta bakin Shugaba – Sha’aibu Musa Jibrin

Ya kara bayyana cewa, ko layi za’a ja, matukar kowace hukumar gwamnati zata biya kason da doka ta bayyana, ko shakka babu za’a rage wahalhalun da ‘yan Fanshon ke fama, duba da tsadar rayuwa, inda yace hukumar SUBEB da Min for LG sune ke kan gaba wajen rike kudaden

Hukumar Fansho na bin SUBEB fiye da Naira biliyan Talatin da Uku (#33bn) inda Hukumar Min for LG ke biye da bashin fiye da Naira biliyan Goma sha Daya (#11bn) inda Jami’ar kimiyya da fasaha ta Wudil, Wreca, Water Board da Internal Revenue ake binsu fiye da (#9bn)

Sha’aibu Musa Jibrin yayi kira ga hukumomin gwamnati su dubi Allah su sauke nauyin da Allah ya dora a kansu, domin kuwa duk ma’aikaci karshensa dai hukumar Fansho, idan ta gyaru kazo ka iske ta lfy, idan ta back kaima ka shiga cikin masu kokawa.

Daga karshe yayi addu’ar Allah yai wa shugabanninmu jagora, ya basu ikon sauke nauyin da ke kansu, Allah ya taimaki yan Fansho ya fito ma su da hakkokinsu tun suna raye, ya roki Allah wadanda su ka mutu cikin bakin cikin wannan yanayin Allah ya gafarta ma su.

qalubale.news.blog

Gadojin Kano

Daga Bello Muhammad Sharada:

Kusan wata guda da ya gabata, gwamnan jihar Kano Dokta Abdullahi Umar Ganduje ya ziyarci shugaban kasa Muhammad Buhari a fadarsa ta Aso Rock. A lokacin da ya kai masa wannan ziyarar ya yi guzuri da hoton sabon tsarin zane na 3D na zanen sabuwar gadar da yake niyyar gina wa a babban shatale-talen gidan mai na NNPC da yake unguwar Hotoro. Wannan randa shi ne mahadar Kano da jihohin da ke makwabtaka da ita ta kudu wato Jigawa da Bauchi har ya dangana da Yobe da Borno. Babbar hanya ce, mai daukar fasinja da kaya.

Gina gadoji a kwaryar birnin Kano yana cikin ayyukan da suke sanya annashuwa ga gwamnan Kano Dokta Abdullahi Ganduje. Yana alfahari da gadojin. Yana daukarsu da muhimmanci. Har ta kai ana yi masa kirari da “Architect of Modern Kano”. Manufar Ganduje a wannan aikin shi ne a rage cunkoso, a saukaka sufuri, a buda wajen harkar kasuwanci don a inganta harajin cikin gida. Wannan shi ne lissafin zahiri, tunanin badini kuma sai shi gugan karfen na Goggo.

A cikin shekara 40 da suka gabata Marigayi Air Commodore Hamza Abdullahi, gwamnan soja na Kano a mulkin Manjo Buhari shi ne ya fara yin gadar sama don masu tsallake titi. Gadar da ya yi ta karfe ce, kuma an yi ta a kan titin Asibitin Murtala. An yi wannan gadar a 1985-86. Kara habaka da yawan jama’a da ababen hawa tun wancan lokaci yana damun Kano kuma wajibi ne hukumomi su duba bukatar hakan don daukar matakin da ya dace. A shekarar 2012 ne tsohon gwamnan Kano Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso ya fara gina gada. Shi a hikimarsa yana so ya magance wahalar da mahaya ke fuskanta a mahadar Kabuga da Gadon Kaya da Gidan Murtala da Batar Sabon Gari. Wannan shi ne bayanin da gwamnati ta yi wa jama’ar gari.

A lokacin da Injiya Rabiu Musa Kwankwaso da mataimakinsa Dr Abdullahi Ganduje suka karbi mulki daga soja a hannun marigayi Kanar Aminu Isa Kontagora, daga 1999-2003 ya yi aikin fadada tituna na Birnin Kano da fasa wasu hanyoyi don su bulle kuma su hade da manyan titunan Kano kuma su bunkasa kasuwanci da sufuri. Wannan shiri shi ne “Urban Renewal Program” wanda aka gudanar da shi a karkashin kulawar Arch Aminu Abubakar Dabo

Akan aikin Kwankwaso Mallam Ibrahim Shekarau ya dora ayyukan gwamnatinsa na “Kano Road Map” wanda ya fadada manyan titunan Kano daidai da na Abuja da Lagos. Ya yi titi daga farkon Zoo Rd har karshensa, ya sake fasalin titin BUK tun daga Kofar Kabuga har Gidan Murtala. Ya zarce da shi daga Gidan Murtala har masallacin Juma’a na Fagge. Ya dauko daga kofar Nassarawa har gidan Gwamna. Ya tashi wani daga Kofar Kabuga har zuwa El Duniya a Kantin kwari.

Bayan Kwankwaso ya dawo a karo na biyu, daga shekarar 2011-2015 sai ya fitar da tsarin gina gadoji. Ya yi Gadar sama a mahadar Gidan Murtala da Titin Obasanjo da kofar Gidan rediyo na Kano. Sannan kuma ya kirkiro Gadar Kasa a Kabuga da Gadon Kaya. Kwankwaso ne ya bada tunani da zanen Gadar Titin Panshekara zuwa Madobi.

Shekara biyu da ya gabata gwamnatin jihar Kano ta aza harsashin gina gadar kasa a mahadar titin Zaria rd da titin Zoo rd. Ana kashe naira biliyan hudu da motsi a wannan aikin. Kafin ya kai karshe zai ci biliyan shida.

Jimlar ayyukan gadoji da Ganduje ya yi na kasa sun zama uku. Daya a kan titin Madobi, daya a kan titin Katsina, sai kuma ta titin Zaria. Sannan kuma ga aikin gadar sama a Sabon Gari kan Murtala Muhammad Way. Ana kan yi sabuwar gada a Asibitin Murtala da Kantin Kwari. Yanzu kuma an bada kwangilar gina gada a NNPC Hotoro akan naira biliyan Tara. In an gama za a gina wata a mahadar da za ta dangana titin Filin jirgin sama na Aminu Kano da titin Katsina Rd.

Da ainihin abin da aka kashe da kiyasin kudin wadannan ayyukan a zamanin Kwankwaso da Ganduje ya doshi naira biliyan 100.Dukkansu babu aikin kasa da naira biliyan biyu.

Anan ne nake da magana. Naira biliyan 100 ba wasa bane. Babu laifi a kashe su, amma “kudi a kashe su ta hanya mai kyau” Aikin gadojin nan “Infrastructure Investment” ne, menene alfanunsa, idan aka kashe su, nawa ake saka rai da tsammanin su jawo na riba? Shin gina titunan yana rage cunkoso ko kuwa kawai ya kara wa Kano kwalliya ne ?

Abu na biyu, shin wannnan manyan ayyukan gadojin shi ne bukatar mutanen birni da akasarinsu ‘yan kasuwa ne da ma’aikata da mata da matasa? Da aka dauki kudaden mutanen karkara aka gina gadoji a birni, haka shi ne dabarar raya jama’ar karkara, wanda akasarinsu manoma ne da kananan ‘yan kasuwa?

A fahimtata wannan ayyukan gadojin ba shi ne bukatar mutanen birni da karkara ba. Da Kwankwaso da Shekarau sun buda hanyoyin Kano na shiga da fita. Babbar matsalar masu bin hanya ko a mota ko a babur ko A Daidaita Sahu shi ne gajen hakuri da karya doka. Wannan kuwa musiba ce babba, gina gada ba zai yi maganinta ba.

Da Aliko Dangote da Bill Gate da Halifa Muhammad Sanusi II sun taba fada cewa Human Capital Development shi ne kashin bayan habakar kowacce kasa. Ma’ana gina ilimi da lafiya da muhalli da samar da aikin yi. Gina gadoji yana zuwa ne daga bisani.

Gwamna Ganduje zai iya ciwo ba shi mai kauri, ya kashe, amma fa a duba ayyukan da suke zasu gina jihar in an yi shi. Wannan kwalliya da kyale-kyale ba sa dorewa, saboda kayan yayi ne. Nan da wani lokacin kankani zamani zai zo a rushe su, a manta da kwalliyar, ginshikin da zai tabbata shi ne wanda aka gina shi na raya dan adam. .

Kano garin kasuwanci ne da noma. Kano gari ne mai albarkar jama’a da damarmaki masu tarin yawa. Me Ganduje ya yi a noma da kasuwanci da sana’a? Ina aka kwana a tashar jirgin kasa daga Kaduna zuwa Kano? Ina aka kwana a habaka tashar tashi da saukar jirgin sama? Ina aka kwana wajen gina Dala Inland Dry Port? Ina aka kwana da Export Processing Zone na Panisau? Ina aka kwana da samar da lantarki a Sharada da Challawa da Bompai Industrial Zone? Ina aka kwana da maganar habaka Commercial da Private Property Development a Kumbotso da Dawakin Kudu da Ungoggo da Gezawa da Madobi?

Ta yaya za a kashe kusan naira biliyan 100 a harkar gina gadoji, amma makarantun firamare da sakandire sai dada lalacewa suke yi? Ilimi ya zama banza a wulakance? Ta yaya sauro da kuda sun gagari kundila?

Ni ban gamsu da ayyukan gada ba. Wannan shi ne fahimtata . Bana goyon bayan cogen gina jiha ta hanyar North Korean Style, na fi gamsuwa da hanyar gina jiha ta hanyar South Korean style.

Shinfida bututun iskar gas zuwa Kano

Gwamnatin shugaba Buhari tayi kokari wajen shimfida bututun iskar gas zuwa Kano, bazamu fasa fadan ayyukan alkhairi da gwamnati ta kawo ko take shirin kawowa arewa ba, haka kuma bazamu daina fadar inda shugaban yayi kuskure ba, masamman a harkar tsaro.

Shima muna sa rai shugaba Buhari zai ji koke-koken al’ummah a gyara domin rashin tsaro a arewa yayi muni dayawa fiye da kowane lokaci, anyi wa manoma yakan rago a Borno wanda ake tunanin yawansu yakai mutane 43 zuwa sama a cewar wasu kafafan yada labarai.

Kungiyar ta’adda ta Boko Haram ta dauki nauyin aikatawa, haka kuma an sace yara a makarantar kwana ta kimiyya da fasaha a Kankara jihar Katsina, wanda yawansu yakai 333 a cewar gwamnatin jihar ta Katsina, inda wasu kafafan yada labarai sukace sunkai 600.

An sami rashin daidaiton bayanai tsakanin gwamnatocin biyu ta jihar Katsina da ta tarayyar Najeriya wajen fitar da sanarwar yawan yaran da aka sace, inda gwamna Masari ke ikirarin su 333 ne inda kuma kakakin yada labarai na shugaba Buhari Garba Shehu yace su 10 ne

Da fari dai ana zaton masu garkuwa da mutane suka sace yaran domin neman kudin fansa, amma daga baya kungiyar ta’adda ta Boko Haram ta dauki nauyin sace yaran, amma gwamnatin jihar Katsina ta karyata hannun kungiyar Boko Haram inda tace tana tattaunawa da wadanda suka sace yaran.

Babban abinda ya bada mamaki shine, an sace yaran a yayin da shugaba Buhari ya fara hutu a mahaifarsa Daura ta jihar Katsina, kamar kilometer 190 tsakanin inda yake a Daura da inda aka sace yaran a Kankara, a yadda masana suka bayyana, wanna ba karamin cin fuska bane.

Haka kuma rahotanni sun bayyana cewa yaran an korasu ne cikin daji a cikin wannan dare kamar yadda ake kora shanu, sunyi tafiyar kafa har wayewar gari amma babu wata tirjiya da suka samu daga jami’an tsaro.

Masana sunce jiragen sama na leken asiri da Najeriya ke amfani dasu wajen gano inda mahara ko yan ta’adda ko masu garkuwa da mutane ko duk wani nau’i na ta’addanci basa iya tashi da daddare, karfe 6 na yammacin kowace rana ake sauke su kasa sai wata safiyar kafin su sake tashi

Idan hakane, ta yaya za’a iya gano mahara ko yan ta’adda yayin da suka aikata barna a cikin dare, ma’ana dai sai sunkai inda zasu buya kafin daga baya jami’an tsaro su fara nasu bincike wanda zai basu wahalar gaske kafin su fahimci inda suke boye.

Da alama suma maharan ko yan ta’addan suna da wannan bayanan sirrin a hannunsu, shine dalili da yasa suke cin karen su ba babbaka a cikin dare inji wani mai sharhi a talabijin na farin wata wanda ke watsa wani shiri na Idon Mikiya a gidan radio na Vision fm 92.5MHz

Dan jarida Shu’aibu Mungadi yace, shin wadanda suka siyo wadannan jiragen sama masu leken asiri ba su san jiragen basa iya tashi cikin dare domin gano mafakar ayarin yan ta’adda bane kokuwa menene dalili da yasa suka siyo jiragen?

Lallai ya kamata zuwa yanzu, shugaba Buhari ya aje duk wani aiki na raya kasa ya debi kudin ya zuba a harkar tsaro a siyo jiragen saman leken asiri na zamani domin ayi maganin ta’addancin dake faruwa a kasa baki daya,.

Duk wani aikin raya kasa da gwamnati zata aiwatar bazai isa ga al’ummah ba idan ba tsaro, ballantana su more ko su sharhi romon dimokaradiyya, duk da haka zamu yabawa shugaba Buhari indai a wannan karin zai waiwaya arewa ya magance mana abubuwan da suka damemu.

Masamman fatara da talaucin da suke sa matasa shiga harkar ta’addanci a yanki arewa, ko shakku babu tattalin arewa ya karye rugu-rugu, aikin bude tashar ruwa ta tsandauri da jawo bututun iskar gas zasu taimaka.

Haka kuma ayi kokari a jawo teku zuwa arewa, a hako man fetur da iskar gas da sauran ma’adinai irin su zinare da ke jibge a karkashin kasar arewa, wanna zai tabbatar da tattalin arziki ya dawo arewa, shugaba Buhari zai bar tarihi a matsayin shugaban dake da kishin yankin sa.

Shugaba Buhari ya bude kan iyakokin kasar guda 4 bayan da ya kulle su shekara daya da ta wuce, shima ci gaba ne amma shugaba yayi hakuri a shigo da kayan abinci masamman shinkafa domin a bari kasuwa ta tantance tsakanin ta gida da ta waje wajen yin gogayya da farashi da inganci.

Daga karshe, muna taya shugaba Buhari tare da iyalinsa murnar cika shekaru 78 a raye, muna fata Allah ya karo masa shekaru masu albarka cikin imani da tausayi da karbar shawarwarin da zasu kawowa yankin arewa da kasa bakidaya alkhairi da ci gaba.

http://qalubale.news.blog

Gratuities: Governor Zulum Releases N12bn to 4,862 Borno Retirees

Borno State governor, Prof. Babagana Zulum, on Tuesday announced the release of N12 billion to clear gratuities owed 4,862 retirees who left the state and local government civil service from 2013 to 2017.


Flagging off the payment with symbolic presentation of cheques to some retirees on Tuesday at the Government House in Maiduguri, Mr Zulum explained that the fund was obtained through a loan provided by the Zenith Bank.


The governor recalled that in June and September 2019, the state government had released N3 billion to clear gratuities of 1,684 retirees who left the civil service between 2013 to 2019, at lower ranks, mostly clerks, drivers and messengers.


Mr Zulum noted that while N12 billion was not enough to settle backlog of gratuities, appreciable number of retirees, almost 5,000, would be cleared this time around.

He, therefore, appealed to those who would not be part of the N12bn batch to be patient, saying that the state government was working on settling all gratuities as soon as possible.


“The accumulated backlog of gratuities over the years has been worrisome to successive administrations.

We are making frantic effort to settle all outstanding gratuities and pension arrears of our retired Civil servants. “We decided to take far reaching decision to reduce the waiting by retired state and local civil servants in the State.

We hope this N12b will reduce poverty and stimulate the economy,” Mr Zulum said.


Speaking on issues of pension, the governor explained that from May 2019 to date, a total of 770 complaints were received out of which 650 were rectified and already enjoying their pension while awaiting their arrears to be paid soon.


Mr Zulum also recalled that the state government had recently completed the rehabilitation of Musa Usman Secretariat, including provision of furniture, assuring his administration’s commitment to sustain the payment of retirement benefits to pensioners as at when due. 

The governor announced that the state government had commenced the automatic migration of retirees from salary to pension since May, 2020, disclosing that, so far, over 900 retirees had benefited from the process.

YAKAMATA GIDAJEN REDIYO SUYI GYARA

Daga Umar Faruq Muhammad

Yanzu nake karanta rubutun Mal. Asim Kurawa gameda yadda wani gidan Rediyo yabada labarin Fyade ga wata Yarinya tareda sanya sautin Yarinyar tana fayyace yadda abin yafaru, Yayi rubutun ne don bayyana Illar da Kafafen Labarai ke yadawa da sunan bada Labari.

Nadade ina jin takaici irin yadda Gidajen Rediyo musamman masu zaman Kansu ke azarbabin yada munanan Labarai, magana ta gaskiya akwai kusakurai sosai a yanayin yadda suke yadawar.

Idan mukayi la’akari zamuga yada labaran basa taka rawa wajen kaucewa barnar da akayi sai dai ma tazama kamar koyarwa ga wasu.

Akwai wata kafar Labarai data bada labarin wani Dan Sahu da ya gudu da kayan wasu Mata wanda a karshe Yan sandan Naibawa suka kamashi sakamakon lambar mashin din sa da Daya daga Matan ta haddace, abin mamaki a satin sai ga sabon labarin wani Dan Sahun shima yagudu da kayan wani.

Magana ta Gaskiya yawan yada munanan Labarai sukan zama kamar koyarwa ne ga wasu masu sauraren.

Idan kana bibiyar Gidajen Rediyon mu zakaga kamar Gasa suka dauki harkar Labarai ta irin usulubin dasuke yin Labaran, shiyasa basu fiye la’akari da sakamakon abinda suke yadawa zai haifar ba.

Munada kwararrun Matasa a Gidajen Rediyo, kuma sunada Ilmin Addini daidai gwargwado, ina fata zasu kara dagewa wajen bada shawarwari ga Gidajen su don kaucewa Yada Fasadi.

“KADA KUYADA BARNA A BAYAN KASA”

Ra’ayin Mawallafi: Barazanar da Kudancin Najeriya ke wa Arewa

Yankin Arewacin Najeriya da ke da fadin kasa da arzikin al’ummah da ma’adinai da ke jibge a karkashin ilahirin Arewa wanda shugabannin mu su ka kasa amfani dashi wajen ciyar da yankin gaba, yana samun barazanar wariya daga sauran sassan kasar.

Yanzu dai ta tabbata Arewa bata da katabus a idon abokan zamanta na sassan kasar, masamman Kudanci, wane dalili yasa motsi kadan ake mana kallon kaska duk da irin dimbin al’ummah da fadin kasa da kuma ma’adinai dake jibge a karkashin kasar ta Arewa?

Shugabannin mu na Arewa da suka rike mulkin kasa a wannan karni basu kwatanta halin shugabannin baya ba, basu maida hankali wajen gina al’ummah da tattalin arzikin Arewa ba, shine dalilin da talauci da jahilci suka mamaye Arewa, wannan ya haifar mana da rashin tsaro.

Ba wani motsi da dan Arewa zai yi sai ya sami qalubale daga yan Kudu wajen neman a raba kasar, sun gaji da zama da mu, wannan ya zama kamar wata tsokana da akewa yan Arewa.

Badan lalacin matasan mu ba da rashin maida kai wajen neman ilimi, Arewa daidai take tayi gogayya da kowace nahiya, amma mun kasa daidaita kawunan mu, wannan kuma ya biyo bayan rashin tallafawa daga mahukunta, kowane jinsi yana kokarin tallafawa dan uwansa amma banda hausawa.

Mun zama abin dariya a idon duniya, sai binmu ake ana kashewa kamar beraye, yan kudu su kashemu saboda munje jihohinsu neman abinda zamu rufawa kanmu asiri duk da suma suna shigowa jihohin mu neman kudi, musulunci ne ke mana jagora wajen zama da kowa lafiya a yankunan mu.

Maganar raba kasa taki ci taki cinyewa, wancan mai da yan kudu ke tinkaho dashi, kudadenmu ne aka dauka daga Arewa da muke noma gyada da auduga wajen hakar sa, sai gashi ya zama abin tinkaho da barazana garemu.muna da mai da iskar gas da gwal da glass da sauran ma’adinai a Arewa.

Muna da mai da iskar gas da gwal da glass da sauran ma’adinai a Arewa, meyasa shugabanninin mu na Arewa suka kasa amfani da wannan damar wajen hako wadannan ma’adinai, ko ba komai zamu fita daga talauci, jahilci da rashin tsaro, matukar muka zama masu cin gashin kanmu.

Ba fata muke a raba kasar ba, amma dai a sani cewa idan ma ya kama sai an raba din, ya kasance muna da madafa, abinci da muke nomawa kadai idan an tsaya akansa ya ishemu rayuwa, amma sai gwamnatocin mu sun dage wajen tallafawa aikin tare da jan talakawa a jiki da basu kulawa.

Kulawa na shawarwari da bude mana idanu wajen yasar da lalaci da zaman kashe wando ta yadda zamu dogara da kanmu, ya zama wajibi gwamnonin Arewa su dauki wani tsari na bai daya wajen tabbatar da wannan manufa idan har muna son Arewa ta zauna da gindin ta.

Duk wasu shugabanni daga Arewa da suka taimaki Arewa da ma wadanda basu taimaki kowa ba sai kawunansu, sun sha kwarzaba daga yankin kudu, duk da cewa suma yan Kudun sun yi mulki amma ba wanda ya kwarzabesu, amma duk lokacin da dan Arewa ke mulki sai yasha qalubale daga hannun su.

Mun san shugabannin mu basa mana adalci duk da dauke kai da mukeyi daga garesu, tunanin su din namu ne kuma sun fito daga cikin mu, amma su a karan kansu basa duba haka wajen taimakawa yankin Arewa, muna gani wadanda ke matsa masu lamba sune yan lele a wajensu, mu kuma ko oho.

Shin wannan zai sa a tuna da su anan gaba kamar yadda ake tunawa da magabatansu wadanda suka sadaukar da rayuwarsu wajen kawowa Arewa abinda har zuwa yanzu muke alfahari dashi, irin su Sardauna da Tafawa balewa, wadanda har suka koma ga Allah basu tara dukiya domin amfanin kansu ba?

Ra’ayin Mawallafi: Barazanar da Kudancin Najeriya ke wa Arewa

Yankin Arewacin Najeriya da ke da fadin kasa da arzikin al’ummah da ma’adinai da ke jibge a karkashin ilahirin Arewa wanda shugabannin mu su ka kasa amfani dashi wajen ciyar da yankin gaba, yana samun barazanar wariya daga sauran sassan kasar.

Yanzu dai ta tabbata Arewa bata da katabus a idon abokan zamanta na sassan kasar, masamman Kudanci, wane dalili yasa motsi kadan ake mana kallon kaska duk da irin dimbin al’ummah da fadin kasa da kuma ma’adinai dake jibge a karkashin kasar ta Arewa?

Shugabannin mu na Arewa da suka rike mulkin kasa a wannan karni basu kwatanta halin shugabannin baya ba, basu maida hankali wajen gina al’ummah da tattalin arzikin Arewa ba, shine dalilin da talauci da jahilci suka mamaye Arewa, wannan ya haifar mana da rashin tsaro.

Ba wani motsi da dan Arewa zai yi sai ya sami qalubale daga yan Kudu wajen neman a raba kasar, sun gaji da zama da mu, wannan ya zama kamar wata tsokana da akewa yan Arewa.

Badan lalacin matasan mu ba da rashin maida kai wajen neman ilimi, Arewa daidai take tayi gogayya da kowace nahiya, amma mun kasa daidaita kawunan mu, wannan kuma ya biyo bayan rashin tallafawa daga mahukunta, kowane jinsi yana kokarin tallafawa dan uwansa amma banda hausawa

Mun zama abin dariya a idon duniya, sai binmu ake ana kashewa kamar beraye, yan kudu su kashemu saboda munje jihohinsu neman abinda zamu rufawa kanmu asiri duk da suma suna shigowa jihohin mu neman kudi, musulunci ne ke mana jagora wajen zama da kowa lafiya yankunan mu.

Maganar raba kasa taki ci taki cinyewa, wancan mai da yan kudu ke tinkaho dashi, kudadenmu ne aka dauka daga Arewa da muke noma gyada da auduga wajen hakar sa, sai gashi ya zama abin tinkaho da barazana garemu.muna da mai da iskar gas da gwal da glass da sauran ma’adinai a Arewa.

Muna da mai da iskar gas da gwal da glass da sauran ma’adinai a Arewa, meyasa shugabanninin mu na Arewa suka kasa amfani da wannan damar wajen hako wadannan ma’adinai, ko ba komai zamu fita daga talauci, jahilci da rashin tsaro, matukar muka zama masu cin gashin kanmu.

Ba fata muke a raba kasar ba, amma dai a sani cewa idan ma ya kama sai an raba din, ya kasance muna da madafa, abinci da muke nomawa kadai idan an tsaya akansa ya ishemu rayuwa, amma sai gwamnatocin mu sun dage wajen tallafawa aikin tare da jan talakawa a jiki da basu kulawa.

Kulawa na shawarwari da bude mana idanu wajen yasar da lalaci da zaman kashe wando ta yadda zamu dogara da kanmu, ya zama wajibi gwamnonin Arewa su dauki wani tsari na bai daya wajen tabbatar da wannan manufa idan har muna son Arewa ta zauna da gindin ta.

Duk wasu shugabanni daga Arewa da suka taimaki Arewa da ma wadanda basu taimaki kowa ba sai kawunansu, sun sha kwarzaba daga yankin kudu, duk da cewa suma yan Kudun sun yi mulki amma ba wanda ya kwarzabesu, amma duk lokacin da dan Arewa ke mulki sai yasha qalubale daga hannun su.

Mun san shugabannin mu basa mana adalci duk da dauke kai da mukeyi daga garesu, tunanin su din namu ne kuma sun fito daga cikin mu, amma su a karan kansu basa duba haka wajen taimakawa yankin Arewa, muna gani wadanda ke matsa masu lamba sune yan lele a wajensu, mu kuma ko oho.

Shin wannan zai sa a tuna da su anan gaba kamar yadda ake tunawa da magabatansu wadanda suka sadaukar da rayuwarsu wajen kawowa Arewa abinda har zuwa yanzu muke alfahari dashi, irin su Sardauna da Tafawa balewa, wadanda har suka koma ga Allah basu tara dukiya domin amfanin kansu ba?

Matasanmu na social media sun fara dafe madafun iko

Sau da yawa a yayin zama da mukeyi da jagororin mu, suna fada mana cewa, ya zama wajibi mu tashi mu nemi madafun iko kodai a matakin jam’iyya ko na mulki, daga dukkanin alamu matasan sun yunkuro domin yin amfani da shawarwarin jagororin namu.

Wata rana Sen Ibrahim Shekarau yana fada mana cewa, dukkanin shugabannin da suka mulki kasar Najeriya a lokacin da suka karbi ragamar mulkin, matasa ne, wasu ma idan an kwatanta shekarun mu a wannan lokaci da shekarun su a wancan lokacin da suka karbi madafun iko.

Za’a iske mun girmesu, saboda yawancin su, sun karbi ragamar mulki suna da shekaru 30 ne, ba sukai 40 ba, da alama wannan yayi wa matasa kaimi domin fitowa a wannan lokaci wajen neman kujerun mulki daban-daban, daga siyasar social media ta rikide zuwa siyasar mulki.

Muna rokon Allah, ya dafa wa duk wadanda suka sami nasara wajen karbar tikitin shiga zaben kananan hukumomin su, wadanda basu sami wannan damar ba, muna rokon Allah, ya canja masu da mafifi cin alkhairi.

Daga karshe ina yiwa dan uwan abokin gwagwarmaya Auwal Lawan Aranposu addu’a Allah yabada nasara a zaben da za’a shiga kuma ina rokon Allah, ya bashi Ikon kwatanta adalci a karamar hukumar Nassarawa da sauran yanuwa da abokan arziki da suka sami irin wannan dama.

Ba za’a kammala aikin gina titin Kano zuwa Abuja ba har sai 2025

Bayanai dake fitowa daga bakin ministan ayyuka da gidajen Najeriya Babatunde Fashola yace, titin da gwamnatin tarayya ke ginawa daga Abuja zuwa Kano, ba zai kammala ba sai shekarar 2025, yayin wani taron masu ruwa da tsaki na wasu kusoshin gwamnatin tarayya a Kaduna.

Gidan radio na BBC ne ya bayyana wannan labari a shafinsa, an fara gina wannan titi a shekarar 2018 karkashin gwamnatin shugaba Buhari bisa tabbacin za’a kammala shi cikin sauri duba da irin lalacewar da yayi, ga shi kuma yana lakume rayukan al’ummah sakamakon haddura dake faruwa

Su ma masu garkuwa da mutane su na amfani da wannan dama wajen tare hanya su sace mutane ayi garkuwa da su domin karbar kudin fansa, gwamnati ta kiyasta kashe wa wannan titi kudi naira biliyan dari da hamsin da biyar #155bn.

A gwari-gwari dai zamu iya cewa, har sai Buhari ya kammala wa’adin mulkin sa kafin a kammala titin, duk da matsalolin da titin ke haifarwa a wannan yanki na Arewa ta hanyar rasa rayuka, sace mutane, fashi da makami da ake yi a hanyar, amma sai jan kafa akeyi wajen kammala shi.

Idan gwamnatin shugaba Buhari dan Arewa ta kasa kammala wannan aikin titi a wannan lokaci, wace gwamnati ce zata taimakawa Arewa wajen kammala shi?

http://qalubale.news.blog

BUBA GALADIMA YA ZAGEMU ‘YAN AREWA

By: Abdullahi Sarkin Yakin Apc

Yanzun nan kammala sauraran jawabin da Buba Galadima yayi a cikin bidiyo, inda ya game ‘yan Arewa gaba dayanmu ya kiramu da kalmar shashashu saboda munki tayar da zanga-zangar kamar yadda ‘yan kudu sukayi

Sannan bai tsaya anan ba, Buba Galadima yaci mutuncin Malamin mu shugaban Majalisar Malamai na duniya a kungiyar Izala Sheikh Sani Yahya Jingir, inda ya tuhumi Malam da kokarin bawa shugaba Buhari kariya

Buba Galadima yace su ‘yan Arewa babu abinda suka iya sai batun addini, ana taba mu sai mu kawo addini

Hakika na kara fahimtar cewa wannan rikicin akwai sa hannun manyan miyagun ‘yan siyasa a Nigeria, ba damuwarsu barnan da ‘yan ta’adda masu zanga-zanga ENDSARS sukayi ba, damuwarsu shine mutane 30 da suke karyan cewa wai sojoji sun kashe

Buba Galadima ka zagemu shashashu ba zamu rama ba, amma hakika mu ba shashashu bane, Insha Allahu su Buba Galadima ba zaku ci nasara ba, kuma insha Allahu shugaba Muhammadu Buhari zai kammala wa’adin mulkinsa lafiya

Yaa Allah Ka haramta wa ‘yan jari hujja zuwa kusa da madafun ikon Nigeria

qalubale.news.blog

GANDUJE SUSPENDS MEDIA AIDE OVER ATTACK ON BUHARI

PRESS RELEASE

Governor Abdullahi Umar Ganduje of Kano state has suspended his Special Adviser on Media, Salihu Tanko Yakasai over some unguarded utterances on the person of President Muhammadu Buhari on the social media platform.

The state commissioner for Information, Malam Muhammad Garba, who conveyed the governor’s directive in a statement this afternoon, said the suspension is with immediate effect.

He said that though the media aide has own up the indiscreet comment as his personal opinion, but that as a public figure, it will be difficult to differentiate between personal opinion and official stand on matters of public concern.

The governor therefore warned political appointees and public servants to guard against making statements capable of drawing unnecessary controversy and heating up the polity.

The statement reaffirmed the commitment of Governor Ganduje to the policies and programmes of President Buhari’s administration.

MALAM MUHAMMAD GARBA
Hon. Commissioner, Information, Kano State
11/10/2020

qalubale.news.blog

Ahmad Bamalli Emerges Emir Of Zazzau

Governor Nasir El-Rufai of Kaduna State has announced the Magajin Garin Zazzau, Alhaji Ahmad Nuhu Bamalli, as the 19th emir of Zazzau 17 days after the demise of Alhaji Shehu Idris, the 18th emir of Zazzau.

Bamalli is from the Mallawa dynasty and is Nigeria’s immediate past Ambassador to Thailand.

qalubale.news.blog

Arewa na da albarkatun kasa fiye da kowane yanki a Najeriya

Gwamnan Matawalle kenan, yayin da yake baje kolin danyan zinare wanda ke kwance a jihar Zamfara, inda kuma gwamnatin ta sa ta tono a cikin dan kankanen lokaci.

Albarkatun kasa daban-daban dake kwance a Arewacin Najeriya suna da yawan gaske, matukar gwamnatocin jihohin da irin wadannan albarkatu sukayi amfani da kudaden al’ummar su domin tonowa da sarrafawa domin ciyar da al’ummar su gaba, ko shakka babu zamuyi fice, bawai a Najeriya ba har a duniya bakidaya.

Ko kuma gwamnatin tarayya tayi amfani da kudin kasa domin tonowa, za’a sami karin kudin shiga wacce zata taimakawa man-fetir.

Dattijon Da Ya Rubuta Kur’ani Na Hannu Har Sau Dari Ya Rasu

INNA LILLAHI WA’INNA ILAIHI RAJI’UN

Sheik Bisharah Mustapha masanin Kur’ani dake garin Dafur a kasar Sudan, wanda ya karantar da mutane sama da dubu kur’ani kuma ya rubuta kur’ani na hannu har sama da dari ya rabawa dalibansa kyauta ya rasu yana da shekaru 105.

Allah ya jikansa. Amin.

Source: Rariya

Man Caught With 2,886 ATM Cards Hidden In Packs Of Noodles At Lagos Airport

The Economic and Financial Crimes Commission (EFCC) says it is investigating one Ishaq Abubakar over his possession of 2,886 automated teller machine (ATM) cards. Dele Oyewale, EFCC spokesman, disclosed in a statement on Thursday that Abubakar was apprehended on August 22 by the Nigeria Customs Service (NCS) at Murtala Muhammed International Airport, Lagos state. The […]

Man Caught With 2,886 ATM Cards Hidden In Packs Of Noodles At Lagos Airport

Kano to lockdown

“From Thursday 16th April by 10pm Kano is locked down for the benefit of all in the state. All markets are closed and all public gatherings are banned. The lockdown is for 7 days. We then wait and see what will come up. We are hoping that Allah will see us through,” Gov. Abdullahi Umar Ganduje

Details later

Abba Anwar
Chief Press Secretary to the Governor of Kano State
Tuesday 14th April, 2020
fatimanbaba1@gmail.com

NAJERIYA KASARMU TA GADO

Daga Umar Faruq Muhammad:

In banda tsabagen rashin tausayi da raina hankalin Talakawa, yazaka hana Mutane fita neman Abinci kayi Allawarin raba musu abincin sannan kazo kabasu wannan a Matsayin abinda zasuci su rayu?

Anya kuwa Shugabannin mu suna sane da tsayuwa a ranar Hisabi?

Qalubale@gmail.com

DA DUMI DUMINSA

Majalisar Dokokin Jihar Kano a zamanta na yau litinin 16/3/2020, ta dakatarda yan majalisun kananan hukomin hukumomi kamar haka;

1 Rt. Hon. Isyaku Ali Danja (PDP) Minority Leader (Gezawa Constituency)
2 Hon. Salisu Maje Ahmad Gwangwazo (PDP) (Municipal Constituency)
3 Hon. Labaran Abdul Madari (APC) (Warawa Constituency)
4 Hon. Muhammad Ballo Butu-Butu (APC) (Rimin Gado/Tofa Constituency)
5 Hon. Garba Ya’u Gwarmai (APC) (Kunchi/Tsanyawa Constituency)

Dakatarwar zata dauki tsawon wata shida ba tareda sun shiga majalisa domin wakiltar alummarsu ba. Majalisar kafin yanke hukuncin, ta zargi yan majalisun da tada rigima daidai lokacinda ake zama kamar yadda aka saba.

Idan ba’a manta ba satin daya gabata hargitsi ya tashi tsakanin yan majalisar a lokacinda mataimakin shugaban majalisar ya tashi domin neman sahalewar yan’uwansa akan karanta rahoton tuhuma da ake yiwa Mai martaba Sarki Muhammad Sanusi II mai murabus, wanda hakance ta fusata wasu daga cikin yan majalisar har zaman ya gagara a wannan rana.

Qalubale@gmail.com

Design a site like this with WordPress.com
Get started