ADAM A ZANGO Zaiyi AURE Karo Na shida 6

Fiteccen Jarimin Fina finan Hausa Na Masana’antar “Kanywood” zai Angonce Karo Na shida A ranar Juma’a Mai zuwa da Misalin karfe 2:30pm na Rana a fadar Mai Martaba Sarkin Gwandu dake jahar Kebbi
.
Adam A zango dai yayi aure 6 tun shekara ta 2006 kawo yanzu, Adam ya Auri Matarsa ta farko Amina a shekara ta 2006 kuma ta haifi Yaro mai suna Haidar wanda yanzu shekarasa 12, sai Amaryarsa ta biyu ita ce Aisha ‘yar SHIKA cikin Garin zariya jahar Kaduna wanda ta haifi ‘ya’ya uku 3 Maza
.
Akwai kuma Matarsa ta uku 3 Mai suna Maryam ‘yar jahar Nasarawa, haka zalika ya sake aure na 4 A Lugbe cikin Birnin Yola jahar Adamawa inda ya Auri Maryam AB,
.
Acikin shekara ta 2015 Adam A zango ya karayin Aure a sirrince inda ya auri wata mata mai suna Ummikulsum Mai shekaru 34 A garin Ngaoundere cikin kasar Kamaru kuma ta haifi Yarinya d’aya mai suna Murjanatu
.
Yanzu haka Adam A zango zai sake Angwancewa da Amaryarsa Safiyya Umar Chalawa wacce akafi sani da(Suffy) a ranar Juma’a mai zuwa
.
Bayanai dai sunce yanzu haka Adam A zango bashi da Mata ko d’aya sakamakon Sakinsu da yayi
.
Menene ra’ayinku Gamai da auren Adam A zango?

Published by Ibrahim Ali Ahmed

Political Analyst

Leave a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Design a site like this with WordPress.com
Get started