Majalisar Tarayya Ta Amince Da Kafa Federal Polytechnic, Fagge Kano State

Dan majalisar tarayya mai wakiltar Fagge ya sami nasarar gabatar da wani kudiri a gaban majalisar ta kasa wanda aka yiwa karatu dai dai har uku sannan kakakin majalisar ya buga guduma amincewa baya doguwar muhawara.

Dan majalisar Aminu Sulaiman Goro mai wakiltar Fagge a Jam’iyyar APC Kano, ya bukaci Gwamnatin Tarayya ta kafa makarantar kimiyya da fasaha wato Federal Polytechnic, Fagge inda majalisar ta amince.

Abba K Yusuf Ya Sami Nasara A Kotun Daukaka Kara Ta Kaduna

Wata kotun daukaka kara dake Kaduna inda Abba K Yusuf ya daukaka kara ta yanke hukunci cewa Abba K Yusuf shine halattaccen dan takara a Jam’iyyar PDP

Wannan ya biyo bayan qalubalantar da mai neman takara Ibrahim Ali Amin ya kewa Abba K Yusuf din a wata babbar kotun tarayya a Kano inda alkalin kotun ya yanke hukuncin rashin halattar Abba K Yusuf din sakamakon zargin rashin aiwatar da zaben fidda gwani.

NRC Denies Report Of Train Killing Two In Kano


The Nigerian Railway Corporation (NRC) yesterday denied a report that a train crushed two people to death in Kano.
The Tide had reported that the Police in Kano State on Tuesday confirmed the death of two persons, who were crushed to death by a train in the state capital.
He said, “On April 16, at about 8am the police received a report that two yet-to-be-identified persons, who were stretched out on the railway track, had been crushed to death by a moving train behind Kano Club in Nasarawa Local Government Area of the state.”
But, a statement by AbdullahiAlhaji, the Public Relations Officer of the Zaria District of the corporation on Thursday claimed that some individuals brought out mutilated corpses and placed on the rail track to create the impression of the purported accident.
He said, “On behalf of the Nigerian Railway Corporation management, Northern District, Zaria, I hereby call the attention of the general public, especially people of Nasarawa LGA of Kano State in respect of the train accident that allegedly killed two people in the area.
“Investigations carried out by the District Railway Police Command and Public Relations Officer of the District; reveal that the information transmitted is false as there was no accident on the train.
“However, NRC northern district is of the opinion that the killing was perpetrated by unknown people who came to dump the mutilated corpses on the track to give the impression that they were killed by the train,” he said.
He advised the public to disregard such information that it killed two persons, adding that a train cannot hit and kill a person or persons without traces of blood, flesh or others signs on it.

Ina Muka Dosa

Yayin da wani mai ganganci ya aikata gangancinsa akanka ko akan wani dan’uwanka ko akan dukiyarka, a guje masu kallon abinda ya faru zasu taso suna baka hakuri.

Yayin da aka baka hakuri ma’ana an cutar dakai, kodai cikin ganganci ko cikin rashin sani, amma cikin masu baka hakurin babu wanda zai nunawa wanda ya aikata wannan gangancin laifisa, ballantana kai da aka yiwa gangancin kaji dadin yin hakurin da akeso kayi.

Idan kace baka hakuri ba, sai kuma reshe ya juye da mujiya, sai kuma kazama kaine mai laifi a wajen masu baka hakurin saboda an baka hakuri baka hakura ba.

Wannan shine daya daga cikin Qalubale da muke fuskanta.

ZUWA GA SHUGABANNIN AREWA

Daga Mal Datti Assalafiy

Muna yiwa shugabannin Arewa fatan alheri, zamu yi amfani da wannan damar wajen janyo hankalin shugabannin Arewa akan tashar TV na Arewa24

A takaice dai Arewa24 tasha ce da hukumar leken asiri da tattara bayanan sirrin tsaron duniya (CIA) na Kasar Amurka ta samar ta dauki nauyi ta kawo Nigeria cibiyar Arewa/Musulunci wato Kano ta ajiye domin cimma boyayyar manufarta akan Musulunci da Musulmai

Tashar Arewa24 kyauta ne ake kallo, koma bayan wasu tashoshi irinta da sai an biya kudi, sannan ma’aikatan Arewa24 ana biyansu makudan kudi a matsayin albashi ba tare da sanin ga hanyar da kudin yake fitowa ba

Arewa24 suna gabatar da shiri da yake kayatar da ma’abota kallon tashar, daga cikin abinda suke koyarwa akwai al’adun turawa wanda ya shafi wakoki da rawa, da kokarin kore tarbiyyan yara wanda aka sani na musulunci da al’adun Hausa/Fulani, suna kuma koyar da shiga na banza, suna dusashe hasken ma’abota Littafin Allah Al-Qur’ani Maigirma

Duk wannan abinda Arewa24 sukeyi bai tayar mana da hankali ba, domin muna mayar da alhakkin hakan akan iyayen da suke barin ‘ya’yansu na kallon tashar, amma babban abinda da tayar mana da hankali har muka yanke shawaran ankarar da shugabannin mu don a dauki mataki, shine yadda yanzu Arewa24 suna dab da zasu fara koyar da ayyukan ta’addanci irin na ‘yan Boko Haram da ISIS

Sunyi tsari zasu fara nuna almajiri an daura masa rigar bomb irin wacce masu harin kunar bakin wake suke sakawa a tura su zuwa wani guri zuje su tayar da bomb su hallaka al’umma, kamar dai yadda suicide bombers na Boko Haram da ISIS ke yi, bayan wannan suna tallen yadda tsarin shirin nasu na koyar da ayyukan ta’addanci zai kasance, ta yanda akwai shugaban kungiyar ta’addanci, da kwamandojinsa da masu tsara harin kunar bakin wake, da kuma yadda ake kaddamar da harin ta’addanci a kashe mutane

Ga hotuna nan na daura, idan har shugabannin Arewa ba zasu iya dakatar da tashar Arewa24 ba saboda illoli da sharrinsu, to lallai ya zama wajibi a gargadesu a hanasu yunkurin gabatar da shirinsu na koyar da ayyukan ta’addanci, wannan ya zama wajibi gwamnatin Nigeria ta dauki kwakkwaran mataki saboda a inganta tsaron Nigeria

Iyaye suna ta korafin cewa Arewa24 sun lalata musu tarbiyyan yara, sun koya musu wake wake da raye raye da rashin kunya, to babu shakka kamar hakane zasu koyawa yara ta’addanci har a wayi gari iyaye sun fara korafi kamar yadda suke yi yanzu

Babban abinda nake so na jawo hankalin jama’a shine; yanzu fa akwai wasu abubuwa (ba zan bayyana ba) za’a nuna maka yadda zaka iya kera bomb a dakin dafa abinci na mahaifiyarka, kuma sunce kayan hada abubuwan fashewan yana gewayen gida ba masu wahala bane, to don Allah ya ake tunanin idan an fara nunawa yara kayan hada abubuwan fashewa kamar yadda ake shirin fara koyar dasu yadda za’a saka rigar bomb (suicide vest) a tashar Arewa24???

Muna kira ga shugabannin Arewa da mahukuntan Nigeria su dauki mataki akan Arewa24

Allah (T) muke roko Ya tsaremu Ya tsare mana al’umma daga sharri da makirci da cutarwan Arewa24 Amin

Jirgin Qasa ya Hallaka Wasu Mutane A Kano

Jirgin qasa ya kashe wasu mutane guda biyu (2) a Kano yayin da suke yin bacci akan hanyar wucewar jirgin wacce aka dade ba’ayin amfani da ita.

Wannan lamari ya faru a bayan otel din Kano Club a Karamar Hukumar Nassarawa, mai magana da yawun yan sanda DSP. Abdullahi Haruna shine ya bayyana haka, inda ya gargadin mutane da su guji zama ko kwanciya akan hanyar jirgin qasa.

https://www.vanguardngr.com/2019/04/train-crushes-two-in-kano/

Ana Sami Nasara A Harkar Tsaro

Shugaban sojojin Najeriya Lt Gen Tukur Buratai yace ana sami nasara a harhar tsaro, amma dole sai an hada tsaro da siyasa domin shawo kan ‘yan kungiyar Boko Haram

Buratai yace, an sami damar takaita aikace-aikacen kungiyar ta’adda ta Boko Haram a yankin zirin tafkin Chad da Sambisa

Liyafa Ta Jawo Cece-Kuce

Daga Hon Salihu Sani Sardaunanchedi

Acikin waccan walimar da aka shirya na hango wanda suka ce malam shekarau yayi batan baka tantan saboda ya koma APC na hango wanda suka ce ashe shekarau na siyasa ne dan biyan bukatar kan sa na hango wanda suka ce kada azabe shi wai baida lafiya har ma da y’an wata jam’iyyar na gan su na hango wanda suka buya saida ta nuna suka nuna suna APCn na hango wanda aka tsince su ahanya

Mu kuma da muka karba 100% ko labari bamuji ba duk da cewa anyi mana alkawarin gyara irin wannan abubuwan karfa abari tura ta kai bango

Kada Ka Kuskura Ka Karbo Bashi

Kungiyar kwadago a Najeriya ta gargadi shugaba Buhari da kada ya kuskura ya karbo bashi ko a gida ko a waje.

Sakataren kungiyar Dr Peter Ozo-Eson yayi wannan gargadin cewa, a halin yanzu Najeriya tana da bashi a kanta da yakai naira tiriliyon 24

Na Ajiye Ra’ayin Siyasa

SANARWA DAGA KHADIJA DORAYI

Na ajiye Ra,ayi dakuma duk wani posting na siyasa Bazan lamunci akan wani banxa yaci mutuncina kona Iyayenaba Da kwankwaso da Ganduje Duk tafiyarsu daya
,
Babu wanda nataba gani kona moreshi acikinsu Muntari malumfashine UBANGIDA NA A SIYASA wanda yadauki nauyin karatun,Kanina harya gama,Dan haka duk wanda nabatawa akan siyasa ina rokon sa yayafemin Zandinga postin ne kawai akan abunda yashafi ADDININ MUSULUNCI
,
ALLAH YASA MUDACE

Rikicin Cacar Baka Ta Barke A Fadar Mundubawa

Bayan fitar da wata sanarwa daga wani shafin sada zumunta na facebook da twitter masu lakani da tsohon malamin gwamnan kuma sabon Sanatan Kano ta tsakiya wato Mallam Ibrahim Shekarau Sardaunan Kano.

Wannan sanarwa ta danganta Malam Ibrahim Shekarau da goyawa daya daga cikin masu neman kakakin majalisar dattawa Ahmad Ibrahim Lawan baya, itace ta tada kura tare da baiwa LABBA iska.

Wani tsagin masu baiwa LABBAN iska basu gamsu da sahihancin waccan sanarwa ba, harma suna cewa ba da yawun Mallam Ibrahim Shekarau din aka yi ta ba, a inda daya bangaren ke ikirarin sanarwa sahihiyace kuma da yawun Sardaunan aka yi ta.

Ya zama wajibi magoya baya su fahimci siyasa tare da biyayya ga shugabanninsu, haka kuma Shugaban Mundubawa Sanata Mallam Ibrahim Shekarau, ya fitar da wata kafar sadarwa ta masamman wacce zata bayyana sahihin labarai daga bakinsa domin gudun fadawa rudanin cikin gida da magoya baya zasu iya afkawa.

#Qalubale

Ta Leko Ta Labe

Kamar yadda wani mawaki yayi wata waka mai suna “Ta Leko Ta Labe” haka suna dalibai masu daukar jarrabawar NECO a Jihar Kano Ta Leko Ta Labe.

Gwamnatin Ganduje ta bakin kwamishinan yada labarai ya shelantawa jama’a biyawa dalibai fiye da dubu 38 Kudin jarrabawar NECO amma yau an wayi gari kwamishinar ilimi tace sai masu credit 5 ciki harda turanci da lissafi.

Wannan ya jawo kace-nace a fadin Jihar Kano, inda masu adawa da Gwamnatin suka fara tumurmusarta.

An Fara Qalubalantar Nasarar Zaben da Ganduje Ya Samu A Kotu

Alhamis, 11/4/2019 ita ce ranar da Jam’iyyar PDP da dan takarar gwamna a Jihar Kano Engr Abba K Yusuf suka fara qalubalantar nasarar da Maigirma Gwamna Abdullahi Umar Ganduje yayi.

Wannan ya biyo bayan da hukumar zabe mai zaman kanta ta ayyana Gwamna Ganduje da lashe zaben. Jam’iyyar PDP da dan takarar ta na gwamna Abba K Yusuf sun shigar da koken su bisa dogaro da tarin hujjojin da su ka tattara a gaban alkalai masu sauraron koke-koken zabe wadanda ke zaman su a harabar babban kotun ta Jihar kano.

#Qalubale

Israel Converts Historical Mosque Into A Bar

The Israeli municipality in Safed has turned Al-Ahmar Mosque into a bar and events hall, Al-Quds Al-Arabi reported yesterday.

As one of the most historical mosques in the Arab city, which was occupied by the Jewish gangs in 1948, the building was first turned into a Jewish school, then into a centre for Likud’s elections campaigns and then into a clothes warehouse before finally being converted into a nightclub.

The London-based newspaper reported that the mosque was turned to a bar and wedding hall by a firm affiliated to the Israeli municipality. Its name was changed from Al-Ahmar Mosque to Khan Al-Ahmar.

Khair Tabari, secretary of Safed and Tiberias Islamic endowment, said that he had been waiting for the Nazareth court to take a decision regarding a complaint he filed requesting the evacuation of the mosque and returning it to the endowment.

He said he attached documents to prove Islamic ownership of the mosque. He called for the different political and popular bodies to increase their cooperation with him in order to save the mosque from violations.

Safed was once home to 12,000 Palestinians who were forced out of their homes in 1948.

Tabari said that the mosque is now open for use for everything except prayers by Muslims.

A ILMIN GADO AKWAI ABIN DA AKE KIRA: MAS’ALAR DAN’UWA MAI ALBARKA, DA MAS’ALAR DAN’UWA MASH’UMI

Dr. Ibrahim Jalo Jalingo

1. A cikin Ilmin gado akwai abin da Malamai ke kira “Mas’alar Dan’uwa Na jini Mai albarka”, da kuma “Mas’alar Dan’uwa Na jini Mash’umi”.

2. Misalin Mas’alar Dan’uwa Na jini Mai albarka shi ne:-
Namiji ne zai mutu sannan ya bar magada kamar haka:
– ‘Ya’yansa mata biyu wadanda ya haifa da kansa.
– Jikarsa wacce dansa na tsatso ya haifa.
– Jikansa wanda dansa na tsatso ya haifa.

A nan sai a raba dukiyar da ya bari kashi 6 sai a dauki kashi 4 cikin shidan watau thuluthi biyu nata a ba wa ‘ya’yansa mata biyun. Abin da zai rage shi ne kashi 2 cikin shida na dukiyar, to sai a dauke su a ba wa diyar dansan, da kuma dan dansan. Su kuma sai su raba su zuwa kashi 3 macen ta dauki kashi 1 shi kuma namijin ya dauki kashi 2.

Da ba don wannan dan’uwa nata namijin ba to da ba ta sami kome ba; saboda gwaggwaninta tuni sun riga sun dauki thuluthi biyun da da ma shi ne kaso mafi yawa da mata ke iya samu a matsayin faradhi watau rabo.
Saboda wannan alheri da wannan dan’uwa nata ya kawo mata na samun gado shi ya sa Malaman gado suke kiran shi da sunan “Dan’uwa Mai Albarka”.

3. Misalin Mas’alar Dan’uwa Na jini Mash’umi shi ne:-
Mace ce za ta mutu ta bar magada kamar haka:
– Mijinta.
– Yar’uwarta shakikiya watau wacce suke uwa daya uba daya.
– Dan’uwanta Li’abi watau wanda suke uba daya kawai da ita.
– ‘Yar’uwarta Li’abiya watau wacce suke uba daya kawai da ita.

A nan sai a raba dukiyar da ta bari kashi 2, a ba wa mijinta kashi 1, a kuma ba wa shakikiyarta watau wacce suke uwa daya uba daya da ita kashi 1 da ya rage, ita kuma li’abiyarta, da li’abinta ba su da kome cikin dukiyar.

To amma da babu li’abi namijin sai li’abiya macen to da ita li’abiya macen ta samu kason abin da ake kira cikon thuluthi biyu ta hanyar “Aulu”, watau da sai a raba dukiyar kashi 7, a ba wa miji kashi 3, a ba wa shakikiya kashi 3, sannan a ba wa ita li’abiyar kashi 1 da ya rage.

Ke nan wannan dan’uwa li’abin mamaciya ya zan sanadiyyar hana ‘yar’uwarsa li’abiyar mamaciya samun kome daga cikin gadon; saboda wannan dalilin ne Malaman ilimin gado suka sa masa suna: “Dan’uwa Mash’umi”.

Allah Ya taimake mu har kullum. Ameen.

Design a site like this with WordPress.com
Get started