EFCC Ta Gurfanar da Jami’an Gwamnatin Kano

Hukumar yaki da cin hanci da karbar rashawa a Najeriya EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnati dake kula da hanyoyi da cunkoson ababan hawa na Jihar Kano a gaban wata babbar kotu a Kano.

Wannan ya biyo bayan sojan gona da kuma zamba ta hanyar buga takardun daukar aiki na jabu ga Sabi’u Muhammad, Anas Ahmad da Umar Habibu da sunan daukar su aiki a hukumar Karota da SUBEB daki-daki.

Mutanen da aka gabatar gaban mai shari’a Faruk Lawal sun hada da Abduljalal Salisu da wasu mutane hudu, tuni mai shari’a Faruk Lawal yabaka belin su bisa wasu tsauraran matakai kuma ya dage shari’ar zuwa 27 ga watan 6, 2019.

Published by Ibrahim Ali Ahmed

Political Analyst

Leave a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Design a site like this with WordPress.com
Get started