Sarkin Rano ya dakatar da hakiman Kura, Garun Malam da Takai

Ranar litinin 29/7/2019 Majalisar Fadar Sarki Rano ta aikawa wasu hakimai uku (3) takardar dakatarwa bisa rashin biyayya ga Majalisar Sarkin.

Bayan ta karbi bayanan da suka bayar a rubuce na kariya a sakamakon tuhumarsu da majalisar tayi na rashin yin biyayya ga fadar ta Sarkin Rano, majalisar bata gamsu da amsar da suka bayar ba.

Sakamakon haka, majalisar Sarki Rano, ta yanke shawarar dakatar da hakiman kamar haka;

1) Hakimin Kura

2) Hakimin Garun Malam

3) Hakimin Takai

#Qalubale

Published by Ibrahim Ali Ahmed

Political Analyst

Leave a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Design a site like this with WordPress.com
Get started