Ranar litinin 29/7/2019 Majalisar Fadar Sarki Rano ta aikawa wasu hakimai uku (3) takardar dakatarwa bisa rashin biyayya ga Majalisar Sarkin.
Bayan ta karbi bayanan da suka bayar a rubuce na kariya a sakamakon tuhumarsu da majalisar tayi na rashin yin biyayya ga fadar ta Sarkin Rano, majalisar bata gamsu da amsar da suka bayar ba.
Sakamakon haka, majalisar Sarki Rano, ta yanke shawarar dakatar da hakiman kamar haka;
1) Hakimin Kura

2) Hakimin Garun Malam

3) Hakimin Takai

#Qalubale
