Amaryar Sarkin Kano Sunusi II Ta Tare Shekaru Hudu Bayan Daura Aure

Daga El-Hajeej Hotoro Maje

Amaryar Mai Martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II (Wacce ita ce ta hudu) ta tare bayan Shekara hudu da daurin Aure.

An kawo Amarya Gimbiya Sa’adatu Barkindo Mustapha fadar Sarki ranar Asabar yayin da aka yi budar-Kai ranar Lahadi.

Amaryar ba ta dade da kammala jami’a ba a Landan jim kadan bayan an daura auren.

Idan za a iya tunawa Sarki Sanusi II ya auri ‘yar Lamidon Adamawa, Muhammadu Barkindo-Musdafa, a yanayin auren da ba a yi gagarumin shagali ba gami da tara mutane ba a garin Yola, ranar 25 ga Satumbar 2015.

#Qalubale

Published by Ibrahim Ali Ahmed

Political Analyst

Leave a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Design a site like this with WordPress.com
Get started