MEYASA FREEDOM RADIO SUKA HANA DAN BILKI PROGRAM A TASHAR SU?

Daga Umar Faruq Muhammad:

Amsar itace yayi program yasoki Mai martaba Sanusi na biyu.

Nayi wannan tambayar ne ganin yadda Freedom din sukayi wani shiri dasuke nuna cewa Gwamnatin Kano zata kama wasu mawaka saboda sabanin siyasa.

Freedom sun hana Dan Bilki magana a gidan su saboda yataba kimar Sarki, shin Sarkin Birnin Kano kadai ake cin zarafi a tashar su?

Meyasa suka bari ana taba Shaksiyyar wasu alhalin sun hana a taba ta Sarki?

Shin idan labarin kama mawakan Gaskiya ne menene bambancin aikin Freedom dana hukumar tace fina-finai? Kun hana wani kun kyale wasu, Censor ta kyale wani kunce zata kama wasu!

#Qalubale

Published by Ibrahim Ali Ahmed

Political Analyst

Leave a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Design a site like this with WordPress.com
Get started