Daga Umar Faruq Muhammad:

Amsar itace yayi program yasoki Mai martaba Sanusi na biyu.
Nayi wannan tambayar ne ganin yadda Freedom din sukayi wani shiri dasuke nuna cewa Gwamnatin Kano zata kama wasu mawaka saboda sabanin siyasa.
Freedom sun hana Dan Bilki magana a gidan su saboda yataba kimar Sarki, shin Sarkin Birnin Kano kadai ake cin zarafi a tashar su?
Meyasa suka bari ana taba Shaksiyyar wasu alhalin sun hana a taba ta Sarki?
Shin idan labarin kama mawakan Gaskiya ne menene bambancin aikin Freedom dana hukumar tace fina-finai? Kun hana wani kun kyale wasu, Censor ta kyale wani kunce zata kama wasu!
#Qalubale
