WANNAN AI ABIN KUNYA NE!

Daga Umar Faruq Muhammad:

Jiya nake ganin Labarin wani zama da Gwamnatin Tarayya zatayi a watan Satumba don tattaunawa da ‘Yan Kwadago akan karancin Albashi, tattaunawa ta nawa?

Idan Ma’aikatar Labour zatayi amfani da ta Ido tayaya zata kalli Yan Kwadago bayan a baya sun cimma matsaya?

Yanzu don Allah da wanne irin Idanu Gwamnatin Tarayya zata kalli Talakawan kasa musamman Ma’aikata?

Kun samu ‘Minimum wage’ #18,000, a lokacin Buhun Shinkafa #7500, Litar Mai #97, sauran kayan Masarufi da sassaukan farashi.

A lokacin wannan Gwamnatin Shinkafa sai da ta kai #20,000, yanzu tana #14,000+, Gwamnatin da kanta ta maida litar fetur #145 maimakon #97 da ta tarar dashi, yanzu don Allah kuna ganin kun kyautatawa masu ‘minimum wage’ na #18,000 din can?

Magana ta Gaskiya babu alamar Rahama a wannan Matakin, babu wani yanayi dake nuna tausayin talaka cikin wannan tsarin.

A gani na da ku dauki tsarin yaudarar Ma’aikata akan karin Albashi gwara kuce KUN GAZA BAZAKU IYA BA!

Gaskiya nafada muku, in kun dauka kanku, in baku dauka ba mu kuka jawowa abin fada!

#Qalubale@gmail.com

Published by Ibrahim Ali Ahmed

Political Analyst

Leave a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Design a site like this with WordPress.com
Get started