Masu amfani da sim card wajen aikata laifuka sun shiga uku

Daga Datti Assalafiy:

MASU AIKATA LAIFUKA TA HANYAR YIN AMFANI DA LAYUKAN KIRAN WAYA (SIM CARD) SUN SHIGA UKU

Maigirma Ministan Sadarwa na Kasarmu Nigeria Ash-sheikh Dr Isah Ali Ibrahim Pantami ya bayyana cewa mutanen da suke amfani da layukan kiran waya wajen aikata miyagun laifuka za’a fara bin diddiginsu a tsakanin awa daya kacal a kamasu

Maigirma Ministan ya bayyana haka ne jiya Litinin a garin Katsina lokacin da ya wakilci Maigirma shugaban Kasa Muhammadu Buhari wajen kaddamar da National Emergency Toll-Free Number (112), da kuma Katsina State Emergency Communications Center wanda aka gina domin habbaka harkan sadarwa a Nigeria

Maigirma Ministan ya kara da cewa za’a gina cibiyar Emergency Communications Centre a jihohin Nigeria 36, babu wani kuduri da ma’aikatar sadarwa zata kaddamar imba kudirin shugaba Buhari ba wajen habbaka harkan sadarwa, tattalin arziki, da yaki da cin hanci da rashawa da tabbatar da tsaron rayukan ‘yan Nigeria

Maigirma Minista ya tabbatar da cewa nan da awanni 48 za’a rufe duk wani layin waya da ba’a yiwa rijista ba

Muna rokon Allah Ya taimaki Ministan Sadarwa Ya cika masa dukkan burinsa na alheri

Qalubale@gmail.com

Published by Ibrahim Ali Ahmed

Political Analyst

Leave a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Design a site like this with WordPress.com
Get started