Zamu cigaba da rufe iyakokin Najeriya har sai mun cimma yarjejeniya

Shugaban hukumar kula da fasa kauri Col Hameed Ali (mai ritaya) ya bayyana cewa, Najeriya zata cigaba da rufe iyakokin kasar, har sai lokacin da aka bi ka’idojin shige da ficen al’umma da kayayyaki kamar yadda kungiyar kula da tattalin al’ummar Afrika ta yamma (ECOWAS) ta tsara.

Hameed Ali yayi wannan bayani ne a lokacin da yake zagayen kan iyakokin kasar a kan iyakar Idiroko ta Jihar Ogun, yace babu alama kawo karshen rufe kan iyakar a nan kusa har sai an cimma wannan yarjejeniya.

Hameed Ali yana tare da shugaban hukumar shinge da fice ta kasa Muhammad Babandada yayin wannan ziyara.

#SenIbrahimShekarauMedia

Published by Ibrahim Ali Ahmed

Political Analyst

Leave a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Design a site like this with WordPress.com
Get started