Allah wadai da kamfanin wutar lantarki na Kano

Munyi Allah wadai da kamfanin bada hasken wutar lantarki a Kano, wannan kamfani ya durkusar da harkokin yau da kullun na al’ummar Jihar Kano.

Yanzu haka a kowace unguwa bai wuce a basu hasken lantarki na awa 2 zuwa 3 ba a kowace rana, kuma wata na karawa a kawo takardar biyan kudin wutar, mun rasa dalilin da zai hana asa wa kowa meter.

Akwai alamun yin zagon kasa ga gwamnatin Buhari da wannan kamfani yakeyi, domin muna samun labari cewa, a sauran jihohin kudancin kasar suna samun wuta sosai, don haka muna kira a chanja mana masu sayar da wuta a wannan bangare namu na Arewa.

Qalubale@gmail.com

Published by Ibrahim Ali Ahmed

Political Analyst

Leave a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Design a site like this with WordPress.com
Get started