

A rana irin wannan shekaru biyar da suka wuce a birnin Kano ina nufin 9/6/2014 jama’a sunyi zanga -zanga harma da kone-kone domin nuna kyamar nadin Sarki Sunusi Lamido Sunusi II da Gwamnan wancan Lokaci wato Rabi’u Musa Kwankwaso yayi sabanin wanda ya kamata a nada.
Ko shakka babu a wancan lokaci Kwankwaso yayi wa mutane karfa-karfa ya tilasta musu son zuciyarsa, sai gashi tarihi yana neman maimaita kansa, inda Gwamna Ganduje ya raba masarautar gidan biua (5) haka kuma yake tuhumar badakalar kudi da majalisar masarautar tayi wanda zai iya yin tasiri wajen yin awan gaba da rawanin Sarkin.
Gwamna Ganduje yana kokarin saisaita gidan sarautar na Kano domin yayi daidai da bukatun jama’a sai kuma wasu mabiyan siyasar Kwankwaso da masu mu’amala dashi ta harkar jarida da lauyoyi harma da shi kansa Kwankwason ke tunanin wai Gwamna Ganduje nayiwa mutane karfa-karfa inda suke tuhumar manyan Kano da masu fada aji sunyi shiru sun zubawa Gwamnan ido yanayin abinda yakeso.
Wasu ‘yan jarida da lauyoyi suna alakanta rashin zama lafiya a Kano duk da cewa mudai muna zaune lafiya cikin kwanciyar hankali.
Akwai wasu marubuta da sukayi rubutu a irin wannan rana kamar haka;
1) Prince Dan Sardauna
Jun 9, 2014 at 23:07
Ga abin da wani ya turo mana yace:
Billahillazi lailaha illahuwa narantse da alkur ani idan nayi karya kada allah yakaini gobe kuma kada allah yabani abinda nake nema duniya da lahira nakara rantsewa da alkur ani amatsayina na musulmi dan majen kano wanda akace shine sarkin kano ayanzu kudi yabayar yasayi sarautar kano kuma wanda yayi financial kudin shine wannan fitaccen dan kasuwar wato dahiru mangal wadanda akbawa kudin sune kamar haka. Makama. Miliyan dari. Sarkin dawaki maituta. Miliyan dari. Sarkin bai. Miliyan dari. Madaki. Milyan. dari. Sai babar giwar wato governor kwankwaso wanda yasamu rabo mafi tsoka har naira biliyan biyu. Yasubhanallah allah dangirman zatinka kanunamana karshen wadannan azzalumai allah munbarka dasu.
2) Jameel Sabo
Jun 9, 2014 at 01:01
INNA MAMAKIN MASU CEWA SUNAIWA MAIGIRMA GWAMNA TA’AZIYYAR MUTUWAR MAI MARTABA SARKI,
INDAI YA KAMATA AYIWA GWAMNA TA’AZIYYAH TO LALLAI YA KAMATA AYIWA ABUBAKAR SHIKAU TA’AZIYYAR MUTANEN DA HARE HAREN BAMA BAMAI YA HALLAKA
3) Na’Allah Raheemeeb
Jun 9, 2014 at 06:37
It seems so very easy for Governor Kwankwaso to reverse every decision made by a dignitary at will within his jurisdictions, provided that it doesn’t go well with his liking, yet, Governor Kwankwaso feels free to mention his unchallenged, even though it doesn’t go well with humanity, thinking that he holds the ace. Yes, he holds the ace but he doesn’t hold the crowned ace!
When will the ace he holds got to be crowned? The only question to baffles his brain is the populace who were all out to shame holdouts like Kwankwaso to reverse his decision too.
Now, who holds the JOKER?
Duka wadannan marubuta sun nuna kyamar abinda Kwankwaso ya yi na tozarta masarautar Kano a wancan lokaci, don haka Qalubale gareku masu aibata Gwamna Ganduje da masu jawowa Kano fatan tashin hankali daga kan ‘Yan jarida, lauyoyi, magoya bayan siyasar Kwankwaso da mabiya Sarki Sunusi II, ku shiga runbun ajiyarku ku zakulo mana abinda kukayi wanda zai nuna kishin Kano a wancan lokaci.